Kotu ta yankewa Zakara hukuncin kisa a KANO

 

Kotu ta yankewa Zakara hukuncin kisa a KANO

Wata kotun Majasteri da ke da zama a gidan Murtala a birnin Kano, ta umarci wani mutum mai suna Isyaku Shu’aibu, mazaunin unguwar Ja’en da ya yanka Zakaransa.
Tun farko dai wani maÆ™wafcinsa ne mai suna Malam Yusuf Muhammad Ja’en, ya shigar da Æ™ara gaban Kotun, yana mai cewa, Zakaran yana shiga haƙƙinsa ta hanyar hana shi barci da yawan Cara.
Amma koda aka karantowa wanda ake Æ™ara, sai ya ce, gaskiya ne Zakaran nasa na yawan yin Cara, kuma zai yanka shi ne a bikin “Good Friday” don haka ya roÆ™i Kotun da ta sahale masa zuwa ranar.
Mai shari’a Halima Wali ta amince inda ta umarci mutumin da ya killace Zakaran kuma ya yanka shi a ranar Juma’a mai zuwa wato ranar “Good Friday” É—in.

Post a Comment

Previous Post Next Post